Hukumar kula da lafiya matakin farko ta Najeriya PHCDA tace za’a fara aikin gudanar da rigakafin annobar cutar korona nau’in moderna da gwamnatin Amurka ta baiwa Najeriya.
Kungiyar likitocin Najeriya ta fara yajin aiki na sai baba ya gani a jiya litinin 2 ga watan Ogustan 2021 sakomakon rashin ciki alkawarin yarjejeniyar da ta kulla da gwamnatin kasar
Barde yace akan ware naira miliyan 49 ga makarantun sakandare 42 a jihar, da ke da yawan dalibai 16,411 a kasafin kudin jihar a duk shekara, inda ya bayyana hakan a matsayin wata kulalliya ta yin almundahana.
An kafa kwamitin bincike akan mataimakin shugaba da jami'an hukumar gyara hali ta Najeriya a jihar Filato, sakamakon tserewa da wasu fursunoni suka yi daga babban gidan yari da ke jihar.