An samu sarakuna biyu da kowannensu ke zaman fada a matsayin sarkin Kano a lokaci guda. Yayin da Muhammadu Sanusi da gwamnatin jihar ta mayar da ya rika karbar gaisuwa da mubaya’a a babban gidan sarautar, shi kuwa Aminu Ado Bayero, ya rika yin na shi zaman fada ne a gidan sarki dake Nasarawa GRA.
Ingancin iskar da muke shaka kullum yana da tasiri ga lafiyar mu. Sinadarin Sulfor dioxide da sinadarin carbon monoxide suna daga cikin sinadaren da suke gurbata iskar da muke shakka a fadin duniya.
A kasar Kenya, daliban wata makaranta dake kusa da inda ake zubar da shara mafi girma a kasar sun fara dashen itatuwan gora don bunkasa ingancin iska a yankin.
Dambarwar sarauta a masarautar Kano ta sa a karon farko cikin tarihi, an samu sarakuna biyu da kowanne ke zaman fada a matsayin sarkin Kano – kuma a cikin birin na Kano
Farfesa Tijjani Naniya wani masanin tarihi a jami’ar Bayero dake Kano ya yi bayani kan inda dambarwar Kano ta samo asali.
Ana sa ran fitar da cikakken sakamakon zaben a karshen makon nan da mu ke bankwana da shi.
Falasdinawa a birnin Rafah da ke kan iyaka sun ba da rahoton kazamin fada a 'yan kwanakin nan, yayin da sojojin Isra'ila ke kara fadada hare-haren da suke kai wa a kudancin kasar, tare da kwace iko da daukacin iyakar Gaza da Masar.
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana a ranar Juma’a cewa ‘yan aware a yankin kudu maso gabas sun kashe sojoji biyar a wani hari da suka kai a wani shingen binciken ababan hawa.
Mazauna Rafah sun ba da rahoton mummunar luguden wuta da harbin bindiga a yau Alhamis a birnin Gaza mai nisa da ke kudu bayan da Isra'ila ta ce ta kwace wata hanya mai mahimmanci a kan iyakar Falasdinawa da Masar.
A ranar Alhamis ne za a kashe wani mutum mai shekaru 50 da haihuwa ta hanyar yin allura mai guba a jihar Alabama da ke Kudancin Amurka bisa laifin kashe wasu tsofaffin ma'aurata.
An kama wani shugaban ‘yan fashi da makami a Najeriya da ake nema ruwa a jallo da yin garkuwa da jama’a tare da mutanensa 65 a kudancin Nijar, kamar yadda hukumomin yankin suka sanar.
'Yan Afirka ta Kudu sun fara jefa kuri'a a zaben da ake yi wa kallon mafi muhimmanci a kasar a cikin shekaru 30, kuma wanda ka iya daga martabar dimokraɗiyyar ƙasar zuwa wani matsayi.
Yakin da Isra'ila ke yi a Gaza tun bayan harin na ranar 7 ga watan Oktoba ya sake farfado da yunkurin da duniya ke yi na a bai wa Falasdinawa kasar tasu.
Ruwan sama kamar da bakin kwarya da ya biyo bayan wata mummunar guguwa ta haddasa rugujewar wani katafaren rami a jihar Mizoram na kasar Indiya inda ya kashe mutane 12, kamar yadda jami'an gwamnati suka bayyana a jiya Talata.
Hukumomin sun ce "sun zo ne a kan babura kusan 100 kowannensu dauke da mutane uku."
Domin Kari