Gwamnatin tarayyar Najeriya ta baiwa gwamnatin jihar Kano tallafin tireloli 100 na shinkafa, tirelolin dawa 44 da na masara guda hudu domin rabawa ga mabukata.
Wasu mutane hudu da ake zargi da kai harin a dakin raye-raye da wake-wake na kasar Rasha da ya kashe mutane sama da 130 sun gurfana a gaban kotu a birnin Moscow jiya Lahadi bisa zargin ta’addanci.
Biyo bayan umurnin shugaba Tinubu na gaggauta ceto daliban Kuriga sama da 280, babban hafsan tsaron Najeriya Janar Christopher Musa ya ce sojoji sun dukufa wajen ganin an ceto daliban da kuma hukunta ‘yan bindigan da ke wannan aika-aika, da wasu rahotanni
A ranar Juma'a ne Rasha da China suka ki amincewa da wani kuduri na Majalisar Dinkin Duniya da Amurka ta yi kira da a gaggauta tsagaita wuta a yakin Isra'ila da Hamas a Gaza don kare fararen hula da ba da damar kai agajin jin kai ga Falasdinawa sama da miliyan biyu da ke fama da yunwa
Wani rikici tsakanin al'umomi biyu a gabashin kasar Chadi ya yi sanadiyar mutuwar mutane 42, kamar yadda ma'aikatar tsaron jama'a ta sanar a ranar Alhamis, a wani yanki na hamada na babban yankin Sahel dake fama da takaddamar filaye.
Isra'ila za ta karbe iko a Rafah ko da kuwa zai haifar da baraka da Amurka, in ji wani babban jami'in Isra'ila a ranar Alhamis, yana mai bayyana birnin Gaza mai cike da 'yan gudun hijira a matsayin sansanin karshe na Hamas mai dauke da kashi daya bisa hudu na mayakan kungiyar.
Makwanni biyu ke nan Tsholofelo Moloi yana cikin dubban 'yan Afirka ta Kudu da ke yin layi don samun ruwa yayin da babban birnin kasar, Johannesburg, ke fuskantar rugujewar tsarin kayan aikin ruwa da ba a taba gani ba.
A ranar Alhamis ne wani jirgin ruwa na kasar Indonesiya ya gano wani kwale-kwalen katako da ya kife da ‘yan gudun hijira Musulman Rohingya da dama, suka kuma ceto wadanda suka tsira da rayukansu da ke tsaye a kan katakon jirgin.
Domin Kari