A cigaba da nemar maslaha game da takaddamar Sarkin Kano Muhammadu Sanusi (ii) da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, Kauran Bauchi, Gwamna Abdulkadir Bala Mohammed Duguri, ya lashi takobin ganin takaddamar ta kawo karshe.
A Najeriya babbar kotun tarayya da ke Abuja karkashin mai shara’a Bello Kawu, ta umarci hukumar zabe mai zaman kanta INEC da ta mika takardar shaidar nasarar cin zaben da ya gudana a wannan shekarar ga 'yan takarar jam’iyyun PDP, PRP da kuma NNPP, a jihar Bauchi.
Zaben shekarar 2019 yazo da abubuwan ban al’ajabi da kuma mamaki da suka hada har da kwace mulki daga hannayen jam’iyu dake mulki suka koma hannun jam’iyun adawa kamar yadda suka faru a jihohin Bauchi dakuma Gombe da wasu wurare a Najeriya.
An gabatar da wasu kudurori don kyautatawa gwamnan mai barin gado a jihar Bauchi.
A jahar Bauchi ma’aikata da kuma 'yan fensho su na cikin yanayin rudani da kuma rashin tabbas dangane da batun biyansu albashi da kuma hakkokinsu.
Bayan da aka kusa samun tashin hankali a Gombe da safiyar jiya Asabar, hukumomi a Gombe sun yi maza sun kafa dokar hana zirga-zirga daga karfe uku na yamma zuwa kafe shida na safe.
Jama'ar birnin Gombe sun ga wani abin tashin hankali bayan da wasu bugaggu da giya, wadanda ake kyautata zaton jami'an tsaro ne ma, su ka markade 6 daga cikin mambobin kungiyar BB da ke macin Easter a birnin Gombe.
A wani al'amari mai bakanta rai, mutanen jahar Bauchi sun yi rashin wasu bayin Allah wajen 13 a wani hadarin mota, baya ga wasu kuma da su ka ji raunuka.
Bayan kikikaka da ja-in-jar da aka yi ta yi - har da zuwa kotu, a karshe hukumar zaben Najeriya ta ayyana tsohon Ministan Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed Duguri (Kauran Bauchi) na jam'iyyar PDP, a matsayin wanda ya lashe zaben Gwamnan jahar Bauchi.
A jihar Bauchi sake zabukan da ba a akammala su ba a yankunan kananan hukumomin jihar ya gudana cikin yanayi mai kyau musamman ma idan akayi la’akari da samun yawan fitowar mutane masu son kada kuri’a.
A Najeriya hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta tsayar da ranar Asabar 23 ga wannan watan Maris, amatsayin ranar da za a sake zabubbuka a wasu rumfunan zabe da aka samu matsaloli a wasu yankunan kananan hukumomi na jihohi biyar.
Wasu mata magoya bayan dan takarar gwamana na jam'iyyar PDP a jihar Bauchi, Bala Muhammad Duguri (Kauran Bauchi), sun yi wata zanga zangar lumana a kan titin zuwa hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta reshen jihar.
Rahotanni daga jihohin Bauchi da Gombe na cewar zaben gwamna da na 'yan majalisun dokoki a jihohin biyu, yana gudana cikin sauki da kwanciyar hankali kuma ma'aikata hukumar zabe sun isa runfunan zaben kan lokaci har ma suka jira masu kada kuri’a.
Hukumar EFCC shiyyar arewa maso gabas mai shelkwatar a garin Gombe ta kama shugaban karamar hukumar Dukku tare da kansila da suke jihar Gombe bisa laifin sayen kuri’a a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da aka gudanar a yau Asabar 23 ga watan Faburairu 2019.
Domin Kari