Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ziyarar Da Dr. Gummi Ya Kai Rugage Don Kawo Karshen Ayyukan Ta’addanci


A ci gaba da lalaben mafita ga matsalolin rashin tsaro da malamin addinin nan Dr. Ahmad Gummi ya ke yi, ya hadu da shugabannin al'ummomi a Sakkwato inda suka tattauna hanyoyin samar da maslaha ga wadannan matsalolin.

Manufar wannan ziyara a rugaggen fulani ita ce malamin ya hadu da masu ayukkan ta'addanci don jin korafe-korafensu kana ya yi masu nasiha, sai dai a lokacin ziyarar ta Sakkwato ba'a samu haduwa da ‘yan bindigan ba.

Daya daga cikin wakilan ayarin ne ya yi magana da Fulanin da suka hadu don tattaunawa abin da ya ba su kwarin gwiwar furta wasu kalamai.

Daga nan malamin Dr Ahmad Gummi ya yi masu bayanin manufarsa.

Prof. Usman Yusuf tsohon sakataren asusun kula da kiyon lafiya cikin rahusa na Najeriya yana cikin ayarin malamin a wannan ziyara.

A karshe dai ana sa ran malamin zai hadu da shugaban kasa domin tattauna abubuwan da ayarin nasa ya gano da manufarsa da mafita ga wadannan matsalolin.

A saurari rahoton cikin sauti daga Muhammadu Nasir:

Ziyarar Da Dr. Gummi Ya Kai Rugage Don Kawo Karshen Ayyukan Ta’addanci
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:05 0:00


XS
SM
MD
LG