Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yan Gudun Hijirar Sudan A Chadi Na Fuskantar Hadarin Rasa Agaji - MSF


Ana kula da lafiyar yan gudun hijirar Sudan a Chadi
Ana kula da lafiyar yan gudun hijirar Sudan a Chadi

Dubban 'yan gudun hijirar Sudan da suka tsere zuwa kasar Chadi domin gujewa fada a kasarsu na iya fuskantar katsewar tallafin jin kai da magunguna yayin da damina gabatowa, in ji kungiyar agaji ta Medecins Sans Frontieres (MSF).

Sama da mutane 100,000 ne suka tsallaka kan iyaka zuwa kasar Chadi tun bayan barkewar rikici a Sudan a watan Afrilu, kuma adadin na iya rubanya nan da watanni uku masu zuwa, in ji hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (UNHCR) a farkon wannan watan.

Shugaban tawagar MSF a kasar Chadi, Audrey van der Schoot, ya ce ambaliyar ruwa da ke faruwa a wannan lokaci na iya mayar da 'yan gudun hijira saniyar ware da kuma al'ummomin da ke karbar baki a yankin gabashin Sila na kasar Chadi da kuma wasu yankunan da ke kan iyaka da Sudan.

Har ila yau ruwan sama zai kawo hatsarin kamuwa da cututtuka masu yaduwa, idan aka yi la’akari da rashin samun ruwa mai tsafta da tsaftar muhalli, in ji ta.

"Muna fargabar cewa da ruwan sama mai zuwa, mutanen wannan yanki na kan iyaka za su makale, kuma a manta da su," in ji ta, tana mai cewa ana ci gaba da shigowa daga Sudan.

Kusan 'yan gudun hijira 30,000 ne a Sila, inda ba su da matsuguni, ruwan sha da abinci, saboda karancin agajin jin kai. Da yawa sun koma tare da iyalai masu masaukin baki a sakamakon haka, suna matsa lamba kan albarkatun da ba su da yawa, in ji MSF.

Daya daga cikin kasashe mafi talauci a duniya, kasar Chadi ta riga ta karbi bakuncin 'yan gudun hijira kusan 600,000 kafin rikicin Sudan na baya-bayan nan.

Hukumar UNHCR ta ce kasar Chadi na bukatar dala miliyan 214.1 domin samar da muhimman ayyuka ga mutanen da suka rasa matsugunansu a kasar da ke tsakiyar Afirka, wanda kashi 16% ne kawai aka ba da tallafi a farkon watan Yuni.

Rikicin kasar Sudan dai yana shafar 'yan kasar Chadi, yayin da wadanda ke zaune a kusa da kan iyaka ba su da damar samun kiwon lafiya da kasuwanni a Sudan. Wannan ya sa farashin abinci da kayan masarufi yayi tashin gwauron zabi a yankunan da tuni ke fama da matsalar rashin abinci mai gina jiki, in ji MSF.

XS
SM
MD
LG