Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Mutane Tara Suka Kuma Kashe Guda A Yakawada, Jihar Kaduna


‘Yan Bindiga sanye da kayan sojoji
‘Yan Bindiga sanye da kayan sojoji

Kwanaki kadan da sakin Sadiq Ango Abdullahi, daya daga cikin 'ya'yan shugaban kungiyar dattawan Arewachin Najeriya, Farfesa Ango Abdullahi, wasu 'yan bindiga sun sake sace wasu dangin Farfesan a mahaifarsa ta Yakawada da ke karamar hukumar Giwa, Jihar Kaduna.

KADUNA, NIGERIA - Da daren Talatar da ta wuce ne 'yan-bindigan su ka afka wa garin Yakawada da ke karamar hukumar Giwa inda su ka sace mutane tara sannan su ka harbi mutane uku har daya daga ciki ya rasu, a cewar daya daga cikin al'ummar yankin.

Kafin sace mutanen dai an ce 'yan sa kai sun yi kokarin dakile harin, sai dai ba su yi nasarar hakan ba, inji daya daga cikin 'yan sakan da aka yi artabu da su.

‘Yan Bindiga
‘Yan Bindiga

Mun yi ta kiran wayar shugaban karamar hukumar ta Giwa game da wannan hari, to sai dai wayar shi ta na kashe kuma mun tura sakonni amma bamu samu amsa ba har zuwa lokachin hada wannan rahoton. Ko da ya ke dai gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasuru Ahmed El-rufa'i, ya sha nanata bukatar dauki daga gwamnatin tarayya game da wannan matsala ta tsaro.

Kananan hukumomin Giwa, Birnin Gwari, da Igabi dai na cikin kananan hukumomin da ke shiyyar Kaduna ta tsakiya da ke fama da hare-haren 'yan-bindiga da sauran matsalolin tsaro baya da wasu yankunan kudancin Kaduna.

Saurari cikakken rahoton Isah Lawal Ikara:

‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Mutanen Tara Suka Kuma Kashe Guda A Yakawada na Jihar Kaduna.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:37 0:00

XS
SM
MD
LG