Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yajin Aikin Likitocin Najeriya Ya Ya Janyo Koma Baya A Yaki Da Annobar Korona


Yajin aikin Likitocin Najeriya ya tarwatsa tsarin kiwon lafiya a yayin da ake fama da annobar Covid-19.

Likitoci a Najeriya na yajin aikin ne saboda rashin biyansu albashi. Amma yajin aikin da kashi 40% cikin dari na ma’aikatan jinya na kasar ya zo ne a yayin da aka sake samun bullar cutar coronavirus, wanda ke kawo cikas ga tsarin kula da lafiya na Najeriya.

NARD, wacce ke wakiltar kusan kashi 40% cikin dari na ma’aikatan likitancin Najeriya, tana nuna rashin amincewa da albashin da ba a biya ba da kuma abin da kungiyar ta ce rashin kyawun yanayin aiki da fa’ida ga membobinta.

Kungiyar likitocin tana kuma zargin hukumomin lafiya na Najeriya da gaza cika alkawuran da aka dauka a farkon wannan shekarar don biyan wadannan bukatu. Wadannan alkawuran sun sa kungiyar ta janye yajin aikin a watan Afrilu.

Sai dai kuma yajin aikin na baya -bayan nan yana tayar da hankali yayin da Najeriya ke fuskantar guguwar coronavirus na uku, wanda ya haifar da mummunan nau’in Delta.

A ranar Laraba da ta gabata, kasar ta ba da rahoton sabbin cututtukan coronavirus sama da 700.

NARD ta ce Likitoci za su ci gaba da yajin aiki sai an biya musu dukkan bukatunsu.

A halin da ake ciki a wannan makon, kungiyar masu ba da shawara ta Likitoci da Hakora ta Najeriya, MDCAN, ita ma ta yi barazanar shiga yajin aiki zuwa ranar Litinin kan albashin mambobinta.

XS
SM
MD
LG