Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

WHO Za Ta Yi Bincike Kan Yanayin Ayyukanta Yayin COVID-19


Tambarin hukumar WHO
Tambarin hukumar WHO

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayyana cewa za ta kafa wani kwamiti mai zaman kansa wanda zai yi bincike kan yanayin kokarinta na shawo kan COVID-19, da kuma irin matakan da su kuma gwamnatoci a duk fadin duniya suka dauka.

Hakan na faruwa ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi matukar sukar hukumar, inda ya zarge ta da zama 'yar koren China.

A ranar Talata ne ma Amurkar ta bayyana cewa za ta fice daga WHO a cikin tsawon shekara daya.

Tsohuwar frai ministar New Zealand, Helen Clark da tsohon shugaban Liberia, Ellen Johnson Sirleaf sun amince su jagoranci kwamitin, a cewar darakta janar na WHO.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG