Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tattalin Arzikin 'Yan Kasuwan Najeriya Na Kara Ta’azzara Saboda Da Takukumin ECOWAS Kan Nijar - Masana


Manyan motoci sun makale a jihar Naija
Manyan motoci sun makale a jihar Naija

‘Yan kasuwar yankin arewacin Najeriya na ci gaba da bayyana zullumi saboda barazanar da dukiyar su ke fuskanta, yayin da iyakokin Najeriya da Nijar ke ci gaba da zama a garkame biyo bayan takunkumin cinikayya da kungiyar ECOWAS karkashin shugaba Tinubu ta sanya akan Jamhuriyar ta Nijar .

Takunkumin tattalin arzikin da kungiyar ta ECOWAS ta sanya wa Jamhuriyar ya yi sanadin dakatar da harkokin cinikayya da kasuwanci a yankin arewacin Najeriya, musamman a jihohi 7 da ke iyaka ta kai tsaya da Jamhuriyar ta Nijar.

A hirar shi da Muryar Amurka, Alhaji Abdullahi Liman Nabuhari daya daga cikin dinbin ‘yan kasuwa a Kano dake safarar kayayyaki tsakanin jamhuriyar Benin, Nijar zuwa sassan arewacin Najeriya yace,

yanzu a Cotonou kayan mutanen Najeriya da suke jibge a tashar sauke kayayyaki ta can sun kai kwantena 2500, sannan wadanda suke iyakar Gaya, wato tsakanin Jamhuriyar Nijar da Benin suna jira a bude boda sun kusa kwantena 2500, baya ga wadanda ke kan hanya suna tahowa”

Tuni dai masana harkokin siyasar kasa da kasa da sha’anin diflomasiya ke cewa, Najeriya na neman shiga sharo ba shanu game da wannan al’amari na sauyin Mulki a Nijar, domin kuwa dokokinta ba su lamunce da hakan ba.

Da yake tsokaci dangane da lamarin, Dr Mansur Datti masanin kimiyyar siyasa da harkokin huldar kasashen duniya ya ce "kudire-kudiren hulda da kasashen ketare na Najeriya ba su lamunci Najeriya ta shiga yaki da kasashen duniya ba, sai dai zata iya shiga yakin wanzar da zaman lafiya, idan kasashen suka samu kan su a cikin rikici.”

Gabanin matsalar takunmin tattalin arziki akan Nijar, Janye tallafin albarkatun mai da gwamnatin Najeriya ta yi da tashin farashin Dala sune suka fara jefa tattalin arzikin arewa dama kasa baki daya cikin wani mawuyacin yanayi a cewar Dr Lawan Habib Yahaya masanin tattalin arziki da hada hadar kudade. Yace “Wadannan abubuwa sune suka sanya matsalar tattalin arzikin arewa dana mutanen arewa ta kara ta’azzara, talauci yana ninkuwa, abinci yana kara yin karanci”

Lamarin ya sa ‘yan kasuwar suka dukufa wajen rokon hukumomin Nijar da Najeriya da-ma shugabancin kungiyar ECOWAS, su kara sassautawa, su sansanta da juna.

Saurari cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:32 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG