Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Syria Ta Bukaci Iran Da Ta Dauki Nauyin Biyan Mayaka


Mayakan dake yiwa Bashar al-Assad yaki tare da goyon bayan Sojojin Rasha sun fito ne daga kasashe daban daban

Gwamnatin Syria ta nemi Iran ta sa kai ta dauki lalurar kula da kuma biyan albashin dubban mayakan Shi’a da ke yaki tareda sojan Rasha a famar da suke na goyon bayan shugaban kasar ta Sham, Bashar al-Assad.

Wata kafar watsa labaran duniyar gizo ta gwamnatin Syria din mai suna Zaman Al Wasel, ne ta ruwaito cewa ta sami wani rubutaccen bayani daga ma’aikatar tsaro inda a ciki ake nuna cewa Syria ta gama yanke shawarar hannunta wa Iran hakkin biyan wadannan dubban mayakan na Shi’a da suka fito daga kasashen ketare daban-daban.

A inda aka fiton nan, galibi akan samu biyan albashin wadanan mayakan ne daga aljihun gwamnatocin Iran din da Syria da kuma na kungiyar Hezbollah ta kasar Lebanon.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG