Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Siyasar Hamayya Ci Gaba Ne Mai Kyau: Dr Sa'idu Ahmad Dukawa


Tutar jam'iyar APC
Tutar jam'iyar APC

Masu fashin baki kan harkokin siyasar Najeriya suna ci gaba da tofa albarkacin bakinsu dangane da zawarcin da shugabannin jam'iyyar APC ke yiwa gwamnoni 7 na PDP wadanda ke takkadama da jam'iyyarsu.

Masu fashin baki kan harkokin siyasar Najeriya suna ci gaba da tofa albarkacin bakinsu dangane da zawarcin da shugabannin jam'iyyar APC ke yiwa gwamnoni 7 na PDP wadanda ke takkadama da jam'iyyarsu. A cikin hirarsu da wakilinmu na Kano Mahmud Ibrahim Kwari, Dr Sa'idu Ahmad Dukawa malami a sashen nazarin kimiyyar siyasa na jami'ar Bayero ya bayyana cewa, idan sabuwar jam’iyar bata yi taka tsantsan ba, tana iya tufkar makaho.

Dr Ahmad yace siyasar hamayya wani ci gaba ne mai kyau kuma abu ne da ake bukata a kowacce damokaradiya, sai dai matakan da yan sabuwar jam’iyar ta APC ke dauka da kuma yadda sauke yi, ya nuna sai kace akwai wata jikakkiya tsakanin wadansu da wadansu, wanda yana iya zama cikas a cikin al’amarin.

Bisa ga cewar Dr Sa’idu, hanyar da suka bi suka ta zuwa wajen gwamnoni dake bisa mulki suka yi watsi da gwamnonin da suka sauka ya nuna sai kace akwai wata jikakkiya tsakanin wadansu ‘yan APC din da wadansu, wanda ba zai haifarwa da APC alheri ba. Yace idan aka tafi haka ba a gyara ba, zai zama sai kace ka toshe kofa daya ka balle daya.

Yace da akwai ci gaban da ake dashi kamar yadda ake yi a Amurka da sauran manyan kasashe inda ake iya amfani da alkaluma na yin bincike a gano yadda daukar mataki kaza zai sa ka cimma buri kaza kayi asarar kaza, da suna da irin wannan, da zasu iya sanin ko matakan da suke dauka zasu kaisu ga cimma nasara ko babu. Amma da yake babu irin wannan damar binciken, kaiwa wadansu ziyara da kuma kaucewa wadansu wadanda sune ‘ya’yan jam’iya yana iya zama da hatsari ga jam’iyar domin wadanda ake zawarcinsu sababbi ne wadanda babu tabbacin zasu amsa gayyatar ko ba zasu amsa ba.

Ga cikakkiyar hirar.
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:39 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG