Shugabannin kasashen Afrika biyar da suka hada da Nigeria, Nijer, Kamaru, Chad da Benin sun halarci wani taron koli da shugaban Faransa Francois Hollande ya gayyata don a tattauna yadda za’a tinkari kalubalen da kungiyar ‘yan tsageran Boko Haram ke tayarwa a kasashen Afrika ta Yamma da ta Tsakiya, musamman a Nigeria. Daya daga cikin manyan batutuwan daaka tabo a taron shine yadda za’a samu hanyoyin ceto ‘yan matan nan sama da 200 ‘yan makaranta na Nigeria da kungiyar Boko Haram din tayi gaba da su a jihar Borno. Kan wannan taron ne, Aliyu Mustaphan Sokoto ya zanta da Seiddik Abba Mamadou, babban editan mujallar “Jeune Afrique” dake can Paris:
Shugaban Faransa ya Jagoranci Taron Kasashen Afrika Kan Boko Haram
![Shugaba Francois Hollande na Faransa, da kuma Shugaba Goodluck Jonathan na Najeriya a kofar dadar shugaban Faransa, Asabar 17 Mayu, 2014.](https://gdb.voanews.com/73b6dd3e-46bd-4664-8fba-7bb7fcf49da8_cx0_cy9_cw0_w250_r1_s.jpg)
Shugabannin Nigeria, Kamaru, Nijer, Chad da Benin sun halarci taro a Paris kan Boko Haram.