Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rikicin Irigwe Da Fulani Ya Yi Sanadin Asarar Rayuka A Filato


Gwamnan Jihar Pilato, Samuel Lalong (Hoto: Twitter @PLSGov)
Gwamnan Jihar Pilato, Samuel Lalong (Hoto: Twitter @PLSGov)

An kashe mutane da dama a wani rikici tsakanin Irigwe da Fulani a karamar hukumar Bassa da ke jihar Filato.

Shugaban kungiyar kabilar Irigwe a karamar hukumar Bassa da ke jihar Filato, Robert Ashi, ya tabbatar da mutuwar mutane hudu da kone gidaje fiye da dari da sare amfanin gona a wani sabon hari a karshen makon jiya.

Rikicin kablinacin a jihar ta Filato facce ke tsakiyar arewacin Najeriya ya Jima yana faruwa.

Sai dai a gefe guda kuwa shugaban kungiyar makiyaya Fulani ta Miyetti Allah Cattle Breeders a jihar, Nura Muhammad ya ce daga ranar Laraba zuwa ranar Asabar an kashe musu mutane Biyar da dabbobi.

A tafi aksarin lokuta, bangarorin biyu kan kai wa juna harin ramuwar gayya, zargin da sukan musanta.

Rundunar da ke wanzar da zaman lafiya a jihar Filato ta ce ta yi namijin kokari wajen hana abin da ta ce taho mu gama tsakanin matasan Fulani da Irigwe.

Kwamandan rundunar, Manjo janar Ibrahim Sallau Ali a wata sanarwa ta hannun kakakin rundunar, Manjo Ishaku Takwa, ya ja hankalin masu ruwa da tsaki daga bangarorin Fulani da Irigwe kan su gargadi matasansu.

Matsalar tsaro a ‘yan kwanakin nan ya kazanta a kananan hukumomin dake arewacin a Filato abin da ya kai ga hukumomin cihar suka kaddamar da was Sabin kayan aiki a 'yan makonnin baya.

Gwamna Simon Lalong ya ce dalilin samar da kayayyakin da suka hada da motoci da basura shi ne, don a magance hare-haren da ake kai wa a sassan jihar.

Saurari cikakken rahoton cikin sauti:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:07 0:00

XS
SM
MD
LG