Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya: An Tura ‘Yan Sanda 2000 Don Su Taimakawa Sojoji a Yaki Da Boko Haram


Nina Stefuryak, anak perempuan berusia 2 tahun, bermain di taman bermain di depan sebuah bangunan yang hancur di distrik Borodianka, wilayah Kyiv, Ukraina, di tengah invasi Rusia ke negara itu. (Foto: Reuters)
Nina Stefuryak, anak perempuan berusia 2 tahun, bermain di taman bermain di depan sebuah bangunan yang hancur di distrik Borodianka, wilayah Kyiv, Ukraina, di tengah invasi Rusia ke negara itu. (Foto: Reuters)

Hedikwatar rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta tura zaratanta kimanin dubu biyu zuwa shiyyar Arewa maso Gabas don yaki kafada da kafada da sojoji karkashin rundunar Operation Lafiya Dole a yakin da ake da mayakan Boko Haram.

Kakakin rundunar ‘yan sanda Mista Jimoh Moshood, ya ce baya ga yakin da ‘yan sandan zasu yi akwai kuma karin rawar da zasu taka, kamar tsare garuruwa da yankunan da aka kwato da samar da tsaro ga jami'an kungiyoyin agaji da kayan agajin da ma kare sansanonin ‘yan gudun hijira.

Rundunar ‘yan sandan tuni ta tura karnukan da aka horas guda dari don wannan yaki, baya ga ‘yan sandan sama da aka tura suna sintiri da jirage masu saukar ungulu.

Zaratan 'Yan Sandan Najeriya Na Musamman
Zaratan 'Yan Sandan Najeriya Na Musamman

Amma wani masanin tsaro kuma tsohon malami a makarantar horas da Hafsoshin sojin Najeriya Dakta Umar Ardo, ya ce shigar yan sandan cikin yakin wannan ba dai dai bane.

Hakan a cewarsa na nuna tamkar sojoji sun gaza ne, domin shekara da shekaru sojoji ke gudanar da wannan yaki, kuma kundin mulkin kasa ma su sojin ya dorawa alhakin wannan aiki.

Domin cikakken bayani saurari rahotan Hassan Maina Kaina.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:25 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG