Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Muna Nazarin Tayin Da Amurka Ta Yi Na Ceto Daliban Kuriga – Gwamnatin Najeriya


Ministan yada labarai, Mohammed Idris (Hoto: Facebook/Ministry of Information)
Ministan yada labarai, Mohammed Idris (Hoto: Facebook/Ministry of Information)

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnati ba za ta biya kudin fansa ba.

Kasashe da dama ciki har da Amurka, sun yi wa Najeriya tayin taimakawa wajen ceto daliban Kuriga da aka sace a jihar Kaduna, in ji Ministan yada labarai Mohammed Idris.

A karshen makon da ya gabata ‘yan bindiga suka far wa makarantar firaimre da saakandare ta Kuriga suka kwashe dalibai sama da 250 a cewar Kamfanin Dillancin Labarai na AFP.

A cewar Idris, gwamnati “na nazari” kan tayin da kasashen suka yi na taimakawa wajen ganin an kubutar da daliban.

Gwamnatin Amurka a cewar AFP, ba ta tabbatar da batun tayin yi ba kuma ba ta yi karin haske a kai ba.

Makarantar firaimare da sakandare ta Kuriga a jihar Kaduna (Hoto: AP)
Makarantar firaimare da sakandare ta Kuriga a jihar Kaduna (Hoto: AP)

Kalaman Ministan na zuwa ne yayin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa ba za ta biya kudin fansa ba.

‘Yan bindigar da suka sace daliban sun nemi a biya su Naira biliyan daya a matsayin kudin fansa.

Matsalar garkuwa da mutane domin neman kudin fansa ta zama babbar matsala musamman a arewa maso yammacin Najeriya inda ‘yan bindiga kan yi garkuwa da mutane da dama ciki har da kananan daliban makaranta.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG