Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Muhimmancin Taron Zuba Jari Da Shugaba Buhari Yake Halarta A Saudiya


Shugaba Buhari (Facebook/Femi Adesina)
Shugaba Buhari (Facebook/Femi Adesina)

Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari ya isa ‘kasar Saudiyya domin halartar taron saka jari domin bunkasa rayuwar al’umma.

A hirar shi da Muryar Amurka, Malam Garba Shehu, babban jami’in yada labarai a fadar gwamnatin, kuma daya daga cikin tawagar Shugaban ‘kasar ya bayyana cewa, taron wanda ya ke hada kan shugabanni na kasashen duniya da masu zuba jari, dama ce ga Najeriya ta tallata kanta da kuma kulla huldar kasuwanci da masu zuba jari.

Garba Shehu yace bisa ga taken taron na bana, "Zuba jari don bunkasa rayuwar al'umma" taron yana da muhimmanci domin burin gwamnati ke nan ganin an inganta rayuwar al'umma. Yace a duniya duka kowa ya san cewa, ana zuba jari domin a fadada kamfani, don a ci riba. abinda kuma a ke so a yi a wannan taron shi ne a jawo hankalin masu zuba jari, su zuba jari don a taimaki al'ummomi wadanda ya ke an bar su a baya kamar Najeriya.

Shugaba Buhari (Facebook/Femi Adesina)
Shugaba Buhari (Facebook/Femi Adesina)

Yace duk fitunun da ake fuskanta a duniya, yake-yake, da ta'addanci babu abin da ya ke haddasa shi face talauci. saboda haka idan za a sami kamfanoni da masu zuba jari su zo su kafa kamfanoni, su bunkasa tattalin arziki, don a taimakawa al'umma su fita daga cikin rashi, marar shi ya samu to wannan shi ne zai kawo zaman lafiya a duniy baki daya.

Kakakin shugaban kasar ya ce kwanan nan shugaba Buhari ya sa hannu a dokar da za ta canza lamuran yadda ake gudanar da harkokin man fetir da suka hada da yadda ake haka da sayarwa da cikinin man fetir a Najeriya wanda aka yi domin ya fadada wanda duk ya ke so ya zo ya zuba jari a kasar.

Ya bayyana cewa a wannan taron, shugaba Muhammadu Buhari zai tallata irin canje canjen da ake samu wajen fadada tono mu'adinai da dokoki da ake yi masu saukaka shigowa jari kuma a fitar da shi ba tare da jinkiri ba.

voahausa.com/a/ziyarar-aiki-da-shugaba-buhari-keyi-a-saudiyya

voahausa.com/a/buhari-ya-tafi-kasar-habasha

buhari-ya-isa-paris-zai-gana-da-macron-kan-matsalar-tsaro

buhari-zai-je-london-taro-daga-nan-zai-duba-lafiyarsa

Saurari cikakken rahoton da Umar Faruk ya hada:

Buhari ya halarci taron zuba jari a Saudiya-3:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:36 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG