Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mayar Da Almajirai Kamar Tauye Hakkin Su ne - In Ji Wata Kungiya Mai Zaman Kanta


Almajiri
Almajiri

Wata kungiyar kula da 'yancin Almajirai da ake kira “Concerned for Almajiris in northern Nigeria” ta koka game da matakan da gwamnonin Arewacin Najeriya suka dauka na mayar da Almajiri zuwa jihohinsu na asali, tana cewa wannan wata hanyace ta tauye hakkin Almajirai.

Shugaban kungiyar Engr. Abdulghafar Onichide ya ce a dokar addinin musulunci ma idan annoba ta bullo a guri shine, to kada a shiga ko a fita, don gudun kada a yada annobar.

Ya kara da cewa a dokar tsarin mulkin Najeriya kowanne dan kasa yana da ‘yancin da zai zauna a ko ina a kasar, "saboda haka wannan mataki da gwamnonin arewacincin Najeriya suka dauka bai dace ba".

Ya ce matakin da gwamnatocin Arewacin Najeriya ya kamata su dauka shi ne raba almajiranci da yawon bara.

Saurari Karin bayani cikin sauti daga Haruna Dauda Biu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:05 0:00


Facebook Forum

XS
SM
MD
LG