Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mayakan ISIS Dubu Biyar Snu Ja Daga A Mosul Kasar Iraqi


Wasu dake ficewa daga yankin Mosul da ya fada hannun dakarun gwamnatin Iraqi
Wasu dake ficewa daga yankin Mosul da ya fada hannun dakarun gwamnatin Iraqi

An bukaci mayakan IS su kamar dubu biyar da suka ja daga a cikin garin Mosul na kasar Iraq da su ci gaba da dagewa wajen yaki, koda kuwa za’a hallaka su a kokarinsu na rike garin.

A cikin wani faifan jawabinsa da aka warwatsa a kafofin duniyar gizo a ranar Talatar da ta wuce ne, shugaban kungiyar da ya aiyyana kansa a matsayin shugaban Musulmin yankin, Abu Bakr al-Baghdadi ne yake musu wannan rokon, inda yake kara da nuna musu cewa mutuwarsu wajen kare akidojinsu yafi kima fiyeda ace sun gudu, sun bar fagen dagar.

Wannan sako daga Baghdadi shine na farko tun cikin watan Desimban bara kuma yana zuwa ne makwanni hudu bayanda sojojin Iraqi da na Kurdawa suka kaddamar da yunkurin sake kwato birnin na Mosul dake karkashin ikon IS tun tsawon shekaru biyu.

Kafofin hukumomin liken asirin Amurka sun ce babu wata hujjar yin tambaba a kan ingancin wannan faifan kuma sun tabattarda cewa ba’a dade da daukar sautin sakon ba.

XS
SM
MD
LG