Mataimakin Shugaban Kasar Misra, Omar Suleiman ya yi watsi da kiraye-kirayen Shugaba Hosni Mubarak ya yi murabus nan da nan, ya ce wannan hanzarin zai haifar da rudami. Wannan jawabin nasa ya zo ne a daidai lokacin da masu zanga-zanga da jefe-jefen duwatsu su ka bijire wa dokar yana yawo a babban birnin kasar, al-Khahira, inda aka yi ta jin karar harbe-harben bindigogi a bisa tituna har zuwa dare. Masu zanga-zangar kin amincewa Mr Mubarak ya cigaba da zama bisa karagar mulki har sai karshen wa’adinsa, sun sha alwashin kaddamar da wata gagarumar zanga-zanga a gobe Jumma’a a yinkurinsu na matsa wa shugaban lamaba ya sauka. Saidai, Mr. Suleiman ya baiyana arangamar da aka yi tsakanin magoya baya da wadanda basu goyon bayan shugaba Mubarak a zaman makarkashiya. Yace babu hannun gwamnati amma za’a gano wadanda suka kitsa wannan makarkashiya.
Mataimakin kasar Masar ya ce Saukar Mubarak daga karagar mulki zai janyo rudami
![Mai zanga zangar kin jinin gwamnati yana jifa da dutse a dandanlin 'yanci na birnin Alkahira](https://gdb.voanews.com/3c750eb0-e513-410c-a99b-34bdc7c35eee_w250_r1_s.jpg)
Mataimakin Shugaban Kasar Misra, Omar Suleiman ya yi watsi da kiraye-kirayen Shugaba Hosni Mubarak ya yi murabus nan da nan