Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kazakhstan Za Ta Kara Saka Dokar Kulle Karo Na Biyu


Kassym-Jomart Tokayev, shugaban kasar Kazakhstan
Kassym-Jomart Tokayev, shugaban kasar Kazakhstan

Gwamnatin kasar Kazakhstan na nazarin kakkaba dokar kulle a ranar 5 ga watan Yuli bayan da aka kara samun adadin masu kamuda da cutar a kasar.

Wannan ne karo na biyu da kasar za ta shiga yanayi na kulle sakamakon Cutar Coronavirus.

Wata kasuwar nama a Kazakstan yayin da ake kokarin fesa magani domin hana yaduwar Covid-19
Wata kasuwar nama a Kazakstan yayin da ake kokarin fesa magani domin hana yaduwar Covid-19

Shugaban kasar Kassym-Jomart Tokayev ne ya bayyana wannan matakin kuma ya ce wata hukuma ta musamman za ta stara yadda za a fara kullen.

Tokayev ya umarci gwamnatinsa da ta kara karfafa matakan takaita yaduwar cutar bayan da adadin masu cutar a kasar ya ninka sau bakwai jim kadan bayan an cire wasu matakai a tsakiyar watan Mayu.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG