Washington, Dc —
Abinda ya dauki hankalin shirin a wannan makon shine fadi tashin da mata ke yi a gidan aure da ba safai a ke yin magana a kai ba, kuma sau da dama, matan da ke ta-maza su ga sun rufawa gidajen aurensu asiri, ba a san suna yi ba balle a yaba masu.
Wannan makon shirin ya yi hira da Fatumatu Mohammed Watara, wata mace a kasar Ghana da ta sami kanta a cikin irin wannan hali tun daga tashinta har a gidan aurenta.
Saurari shirin domin karin bayani:
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.