Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

KALLABI: Koma Baya Da Mata Suka Samu A Zaben Najeriya, Afrilu, 02, 2023


Shirin Kallabi
Shirin Kallabi

Koma bayan da mata suka samu a zaben da aka gudanar a Najeriya na ci gaba da daukar hankalin mata da masu kula da lamura a kasashen nahiyar Afrika da ma duniya baki daya. Wani yanayi da matan suka hanga da ya sa su ka yi ta gangami da fafatukar jan hankalin hukumomi da masu ruwa da tsaki bayanda Majalisar Dattawan Najeriya ta yi fatali da kudurin da zai ba mata kaso talatin da biyar na mukaman gwamnati kamar yadda gwamnatin kasar ta alkawarta.

Banda wannan batun, shirin ya kuma yi hira da Kallabi a fannin wasannin fina-finai da wakoki a Jamhuriyar Nijar, Rashida Alfaharin mawaka, a fannin kiwon lafiya kuma mun haska fitila kan Kaciyar mata.

Saurari cikakken shirin da Grace Alheri Abdu ta gabatar:

KALLABI- Komawa Bayan Da Mata Suka Samu Za Zaben Najeriya
please wait

No media source currently available

0:00 0:25:09 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG