Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Jihar New York Na Shirin Sassaka Mutum Mutumin Ruth Ginsburg


Za a sassaka mutum mutumin Marigayiya mai shari’a ta Kotun Kolin Amurka, Ruth Bader Ginsburg a unguwar Brooklyn inda aka haifeta, abin da gwamnan jihar New York, Andrew Cuomo ya sanar kenan a ranar Asabar da ta gabata.

Ginsburg ta rasu a ranar Juma'a sakamakon matsaloli masu nasaba da wani nau’in cutar ciwon sankara ta ciki, tana da shekaru 87 a duniya.

Mai shari’ar da ke daya daga cikin mata da suka yi fice a fannin shari’a kuma ‘yar rajin kare hakkokin mata, ita ce ta zama mace ta biyu da ta shiga kotun kolin kasar a shekarar 1993.

Ruth Bader Ginsburg
Ruth Bader Ginsburg

Gwamna Cuomo, dan jam’iyyar Democrat, ya ce zai nada wani kwamiti don zaben mai sassaka mutum mutumin da kuma neman wurun da za a a ajiye shi.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG