Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Jihar Neja Ta Tallafawa Matan Fulani


Gwamnan Jihar Neja Ya Bada Cek Ta Tallafi Ga Matan Fulani
Gwamnan Jihar Neja Ya Bada Cek Ta Tallafi Ga Matan Fulani

Matakin bada tallafi ga iyalin Fulanin da ‘yan fashin daji suka raba da shanunsu a Najeriya na daya daga hanyoyin dawo da zaman lafiya a wasu jihohin Arewacin kasar

Gwamnatin jihar Neja tare da hadin gwiwar kungiyar Bago Ruga-Ruga sun dauki nauyin tallafawa matan Fulani da nufin rage masu radadin matsin rayuwa.

Duk da cewa ana zargin kabilar Fulani musamman matasa da hannu dumu-dumu a tabka ta’asar yin garkuwa da jama’a domin neman kudin fansa da satar shanu harma da kisan jama’a babu dalili.

A gefe guda akwai dubban iyalan kabilar Fulanin da suka shiga halin gararamba saboda raba su da dabbobinsu a sakamakon matsalar ‘yan fashin daji.

Matan Fulani guda 100 ne suka samu kashin farko na tallafin Naira dubu dari kowaccensu tare da bude musu wani katafaren dandalin sayar da nono da madara na zamani a tsakiyar kasuwar Minna fadar Gwamnatin jihar Neja.

Hassan Shiroro shugaban kungiyar Bago Ruga-Ruga ya ce ko baya ga wannan tallafi akwai tallafin shanu na musamman ga Fulanin da aka sace ma shanun anan gaba.

Gwamnatin Jihar Neja Da Kungiyar Bago Ruga-Ruga Sun Tallafawa Matan Fulani
Gwamnatin Jihar Neja Da Kungiyar Bago Ruga-Ruga Sun Tallafawa Matan Fulani

Ba da wannan tallafi da sanya cibiyoyin karbar makamai ga Fulanin yafi yin tasiri wajen samar da zaman lafiya a mai maikon yin sulhu da masu rike bindigogin a daji in ji tsohon shugaban miyatti Allah na Najeriya Hardon Paiko da Husaini Yusuf Bisso.

Kwamishinan kula da harkokin makiyaya na jihar Nejan Umar Sanda Rebe ya ce bisa la’akari da yadda matan Fulanin ke dawainiya da iyalai bayan sace shanun mazajensu yasa suka dauki wannan mataki.

Wasu daga cikin matan da suka samu wannan tallafi na dubu 100 sunce zai taiamaka masu wajan bunkasa kasuwancin nono da saida kaji.

Ayanzu dai al’umma na cike da fatar samun saukin wadan nan ‘yan fashin daji masu satar shanun da suka addabi jama’a shekara da shekaru.

Saurari cikakken rahoto daga Mustapha Nasiru Batsari:

Gwamnatin Jihar Neja Da Kungiyar Bago Ruga-Ruga Sun Tallafawa Matan Fulani.MP3
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG