Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Fiye da Daliban Makaranta 300 a Najeriya Sun Sadu da Iyayensu


Fiye da Daliban Makaranta 300 a Najeriya Sun Sadu da Iyayensu
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:40 0:00

Iyayensu daliban.

Damuwa, ba takalma, ga kuma alamar firgita bayan tsawon mako guda a tsare, 'yan mazan makarantar sama da 300, da aka sako bayan sace su a wani hari a makarantarsu, sun hadu da danginsu da Yammacin ranar Juma'a.

Samun sako sama da yara 330 ya faru ne bayan wani martani da gwamnati ta bayar cikin hanzari, wanda ga dukkan alamu sun yi koyi daga satar makarantu mai dumbin yawa da aka yi a baya, musamman ma 'yan matan makarantar Chibok, wanda ba shi da irin wannan sakamakon na farin ciki.

Tashin hankalin ta daliban ta fara ne a daren 11 ga watan Disamba lokacin da wasu mutane dauke da bindigogin AK-47 suka kame su daga makarantar ‘yan maza ta Sakandiren Kimiyya ta Gwamnati da ke kauyen Kankara a jihar Katsina da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.

An tasa su cikin daji kuma aka tilasta masu su kwanta a cikin datti yayin artabun bindiga tsakanin masu garkuwar da sojojin da ke binsu.

Yaran sun bayyana yin tafiya a cikin sunkurun daji da gandun daji daban-daban, tsayawa da rana amma tafiya cikin dare ba takalma, suna taka ƙaya da duwatsu.

‘Yan tawayen masu ikirarin jihadi na Boko Haram a Najeriya sun dauki alhakin satar, suna masu cewa sun kai harin ne a makarantar saboda sun yi imanin cewa ilimin Boko na duniya bai dace da addinin Musulunci ba.

Karin bayani akan: Boko Haram, sojoji, Buhari, Kankara, da jihar Katsina.

XS
SM
MD
LG