Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dukan bangarorin Plato Suna Da Makamai-Kwamiti


Taron shugabannin addinai kan zaman lafiya a jihar Plateau, Nigeria
Taron shugabannin addinai kan zaman lafiya a jihar Plateau, Nigeria

Kwamitin bincike da majalisar dokokin jihar Plato ta kafa domin gano masababin tashe tashen hankali da ake fama da shi tsakanin Fulani da Manoma a jihar ya gano cewa, dukan bangarorin dake kai ruwa rana suna da manyan makamai

A cewar shugaban kwamitin kuma mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Plato,Yusuf Adamu Gardi, kwamitin ya fara aiki kuma ya fahimci cewa, dalilin tashin hankalin nan akan wurin kiwo ne, inda shanu zasu yi kiwo a wurinda bai makata su yi kiwo ba.

Yace akwai wurare-gandun daji-da aka kebe inda aka haramtawa Fulani yin kiwo, wadanda ba a kiwo a lokutan baya, amma yau Fulani suna shiga suyi kiwo, akwai kuma gonakin kabilar Berom da bai kamata a bari dabbobi su shiga ba, wadansu Fulani suna bari dabbobinsu su shiga suyi masu barna.

Haka kuma, zaka tarar wadansu ‘yan kabilar Berom sun kebe wuraren da dabbobi suke wucewa-labi-labi- suna noma a wurin su hana shanu wucewa, yayinda Fulani kuma har wa yau suke barin shanu su shiga lambun Berom suyi masu barna. Wannan yasa ake samun tashe tashen hankali tsakanin manoma da makiyaya kasancewa dukan bangarorin suna da makamai.

Mataimakin kakakin majalisar dokokin yace, bincikensu ya nuna cewa, akwai bindigogi a hannun mutane da yawa, kuma duk inda aka samu makamai da yawa a hannun mutanen da bai kamata ba, za a sami tashin hankali. Dalili ke nan da yace, suna neman shugabannin al’ummomin domin neman hadin kai da goyon bayansu a yunkurinsu na neman ganin an sami zaman lafiya mai dorewa.

Ga cikakken rahoton da wakiliyar sashen Hausa Zainab Babaji ta aiko daga Jos,Najeriya.

Kwamitin Zaman Lafiya a Plato-2:59"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:59 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG