Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Donald Trump Zai Yi Magana Da Buhari Ta Waya


Shugaban Amurka Donald Trump
Shugaban Amurka Donald Trump

Fadar shugaban kasar Amurka-White House ta ce shugaban Amurka Donald Trump zai yi magana da shugabannin Najeriya da Afirka ta Kudu ta wayar tarho a yau Litinin.

Tattaunawar da shugaba Trump zai yi da takwaransa na Najeriya Muhammadu Buhari ya na daukar hankali saboda ba a ji daga Buhari ko kuma ganinsa a bainar jama’a ba tun da ya tafi jinya London ranar 19 ga watan Janairu.

Sabon shugaban kasar Amurka bai yi magana a kan Afrika ko kuma batutuwa da suka shafi Afrika ba tun da ya hau karagar mulki a watan da ya shige.

Babu wani bayani daga fadar White House kan abinda shugabannin za su tattauna a kai.

Bisa ga tsarin aikin Fadar White House, Trump zai tattauna da Buhari da karfe 3:45 agogon Najeriya, kana ya tattauna da shugaban kasar Afrika ta Kudu Jacob Zuma da karfe 5:10.

XS
SM
MD
LG