Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dalilin Kaddamar Da Doka Kan Yin Wa'azi a Kaduna - Shagali


Hon. Aminu Abdullahi Shagali
Hon. Aminu Abdullahi Shagali

Majalisar dokokin jihar Kadunan Najeriya ta kaddamar da dokar hana wa'azi a ko da yaushe.

Majalisar ta ce wannan doka, don hana tashin hankali ne da kuma kariyar jama'a, saboda akwai wadanda ba masana addini bane amma suna wa'azi, a ko'ina kuma suna tayar da hankalin jama'a.

Tsohon kakakin Majalisar dokokin jihar Kaduna Hon. Aminu Abdullahi Shagali, ya ce dokar ta shafi kowane addini, musulunci da addinin krista.

Ya kara da cewa dama dokar nan ta nan tun 1984, amma yanzu an gyara ta ne don a sake samun zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin musulmai da krista.

Ga cikkakiyar hirarsu da wakilin Muryar Amurka Yusuf Aliyu Harande.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:11 0:00

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG