Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dalilin Da Ya Sa PDP Ta Dakatar Da Ayu


Shugaban jam'iyyar PDP, Dr. Iyorchia Ayu
Shugaban jam'iyyar PDP, Dr. Iyorchia Ayu

Dan takarar jam’iyya mai mulki ta APC Hyacinth Alia ne ya lashe zaben gwamna a jihar Benue.

Reshen jam'iyyar PDP a jihar Benue da ke arewacin Najeriya ya dakatar da shugaban jam'iyyar Ayorchia Ayu bisa zargin sa da yi wa jam’iyyar zagon kasa a zaben da ya gabata.

A ranar 25 ga watan Najeriya ta gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin tarayya, kana aka gudanar da na gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi a ranar 18 ga watan Maris.

Matakin dakatar da Ayu na zuwa ne bayan da PDP ta fadi a mazabarsa ta Igyorov da ke jihar Benue a arewacin Najeriya.

Dan takarar jam’iyya mai mulki ta APC Hyacinth Alia ne ya lashe zaben gwamna a jihar Benue.

Yayin da yake karanta wata matsaya da jam’iyyar ta cimma, Sakataren jam’iyyar a mazabar ta Ayu, Vanger Dooyum, ya zarge shi da taka rawa wajen faduwar jam’iyyar a mazabar ta Igyorov da karamar hukumar.

Kazalika jam’iyyar ta ce Ayu bai yi zabe a ranar 18 ga watan Maris ba kuma mafi akasarin makusantansa jam’iyyar APC suka yi wa aiki a zaben.

Jam’iyyar har ila yau, ta zargi Ayu da kin biyan kudin da mambobi ke biya na shekara-shekara.

Kokarin jin ta bakin Ayu kan wadannan zarge-zarge.

Jam’iyyar ta PDP ta ce dakatar da shugaban nata ya fara aiki daga ranar 24 ga watan Maris.

XS
SM
MD
LG