Shaidun gani da ido sun ce fada ya barke a muhimmin birni na Abidjan, tsakanin sojoji da gyauron mayakan da ke biyayya ga hambararren shugaba Laurent Gbagbo. Mazauna wurin sun ce fadan na jiya Talata ya fi tsanani ne a Yopougon da ke gefen birnin Abidjan. Wani jami’in kungiyar agaji ta Red Cross ta gaya wa Associated Press cewa ma’aikatan kungiyar sun gano gawarwaki a kalla 40. Wannan yamutsin ya dada nuna irin kalubalar da kasar ke fuskanta a kokarinta na maido da yanayin tsaro, tun bayan mummunar jayayyar shugabanci tsakanin shugaba Alassane Ouatara, wanda ya ci zaben shugaban kasa da aka gudanar a watan Nuwamba, da kuma Mr. Gbagbo wanda ya ki ya mika ragamar iko. Mr. Ouatara ya amshi ragamar iko a watan jiya bayan da magoya bayansa, tare da goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya da dakarun Faransa, suka kama Mr, Gbagbo a gidansa. Takaddamar shugabanci tsakanin mutanen biyu, ta salwantar da rayukan daruruwan fararen hula, ta kuma raba kimanin mutane miliyan guda da muhallansu.
Dakarun kasar Ivory Coast suna arangama da gyauron mayaka

Shaidun gani da ido sun ce fada ya barke a muhimmin birni na Abidjan, tsakanin sojoji da gyauron mayakan da ke biyayya ga hambararren shugaba Laurent Gbagbo