Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cutar Kwalara Ta Kashe Mutane Da Dama A Kasar Kamaru


Wadansu yara dake fama da Cutar Kwalara
Wadansu yara dake fama da Cutar Kwalara

Cutar kwalara ta kashe mutane da dama a kasar Kamaru, yayinda aka kai daruruwa asibitai da dama. Ana fargaban cewa, an shigo da cutar ne a wadansu wurare daga Najeriya, kuma tana iya bazuwa tsakanin ‘yan gudun hijiran dake gujewa tashe tashen hankalin kungiyar Boko Haram.

Cutar kwalara ta kashe mutane da dama a kasar Kamaru, yayinda aka kai daruruwa asibitai da dama. Ana fargaban cewa, an shigo da cutar ne a wadansu wurare daga Najeriya, kuma tana iya bazuwa tsakanin ‘yan gudun hijiran dake gujewa tashe tashen hankalin kungiyar Boko Haram.

Arabo Saidou, babban jami’in gwamnati mai kula da harkokin lafiya a yankin arewacin kasar Kamaru yace an fara samun rahoton bullar cutar kwalarar ne a kan iyakar kasar da Najeriya kimanin watanni biyu da suka shige.

Yace cutar tana ci gaba da bazuwa tunda aka sami mutane hudu dauke da cutar a garin Mayo Oulo ke kan iyaka da Najeriya ranar agomas ha takwa ga watan Mayu. Yace mutane da dama, musamman kananan yara, suna mutuwa a ciki da wajen asibitai.

A watan Mayu, Hukumar lafiya ta duniya ta buga rahoto cewa, an sami barkewar cutar kwalara a jihohin Adamawa, Borno da Yobe, tun watan Fabrairu, inda ake kyautata zaton kimanin mutane dubu daya da dari shida da sittin da hudu sun kamu da cutar, mutane talatin da daya kuma suka mutu.

Mutane da dama suna shiga kasar Kamaru daga jihohin Adamawa, Borno da Yobe, domin harkokin kasuwanci. Akwai ‘yan gudun hijira akalla dubu dari a Kamaru da suka kauracewa garuruwansu sakamakon hare haren kungiyar Boko Haram, sama da dubu casa’in kuma suna sansanin ‘yan gudun hijira dake Minawao

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG