Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Tabbatar Da Mace Ta Uku Da Ta Kamu Da Cutar Coronavirus A Najeriya


Coronavirus
Coronavirus

Hukumomin lafiya a Najeriya sun tabbatar da killace wata mata mai dauke da cutar Coronavirus. Matar dai ta shigo ne daga Birtaniya a ranar 13 ga wannan watan na Maris, kuma a yanzu haka tana samun kulawa a asibitin da aka killace ta.

Kwamishinan lafiya na jihar Legas, Akin Abayomi ne ya bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai.

‘Yan Najeriya sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta hana sauka da tashin jiragen saman kasashen waje a kasar don dakile bazuwar cutar, wadda yanzu haka ta ke ci gaba da bazuwa kamar wutar daji a wasu kasashen duniya kuma rayuka da yawa na ci gaba da salwanta.

‘Yan Najeriya sun kuma bukaci gwamnatin kasar ta rufe tashoshin jiragen saman ta, ganin cewa kasashe da dama a Afirka sun rufe iyakokinsu tare da haramta yin manyan taruka. Har yanzu dai Najeriya ba ta fitar da irin wadannan matakan ba.

Saurari cikakken rahoton cikin sauti.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:16 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG