Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kashe Wani Babban Masanin Kimiyyar Iran


Inda aka kashe Mohsen Fakhrizadeh a wani gari da ke wajen birnin Tehran a ranar Juma'a, a cewar gidan talbijin din kasar kamar yadda (Fars News Agency ya ruwaito daga AP)
Inda aka kashe Mohsen Fakhrizadeh a wani gari da ke wajen birnin Tehran a ranar Juma'a, a cewar gidan talbijin din kasar kamar yadda (Fars News Agency ya ruwaito daga AP)

Gidan talabijin din kasar Iran ya ce an kashe wani masanin kimiyyar kasar a wani hari da aka kai – mutumin da Isra’ila ta yi zargin shi ya jagoranci shirin kera makamin nukiliyar sojan Iran har zuwa lokacin da aka wargaza shi a farkon shekarun 2000 a cewar kamfanin dillancin labarai na AP.

Ministan harkokin wajen Iran ya zargi Isra’ila da kisan Mohsen Fakhrizadeh a ranar Juma'a.

Amma Isra'ila ta ki ta ki cewa komai kan kisan, Ko da yake, Firayim Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya taba ambatan sunan Fakhrizadeh a wani taron manema labarai.

Gidan Talabijin din kasar ya ce "wasu gungun 'yan ta'adda ne dauke da makamai" suka kai wa Fakhrizadeh hari.

Ya mutu a karamin asibitin bayan da likitoci da ma’aikatan lafiya suka kasa farfado da shi.

XS
SM
MD
LG