Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An kashe mutane 31 a wani hari da aka kai a jihar Borno


BORNO: Harin kunar bakin wake a Maiduguri
BORNO: Harin kunar bakin wake a Maiduguri

Hare Haren kunar bakin wake sun janyo mummunan asarar rayuka da kuma raunata mutane da dama yayinda ake shagulgulan Sallah a Najeriya

Hukumomi sunce hare haren kunar bakin wake sun kashe a kalla mutane talatin da daya a jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya.

Fashewar ta auku ne yau lahadi a garin Damboa. Babu kungiyar da ta dauki alhakin harin nan da nan.

Ana dorawa mayakan kungiyar Boko Haram alhakin hare haren bom da ake kaiwa a yankin a lokutan baya.

Ana dorawa kungiyar Boko Haram alhakin mutuwar kimanin mutane dubu ishirin tun daga lokacin da suka fara tada kayar baya a arewacin Najeriya a shekara ta dubu biyu da tara. Kungiyar mai kaifin kishin Islama tace tana so ta kafa shari’ar musulunci a arewacin kasar da galibi Musulmi ne.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG