Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

AMURKA: Tana Tababan Sahihancin Ikirarin Kungiyar ISIS


Wurin da aka kai hari a Garland, Texas
Wurin da aka kai hari a Garland, Texas

Fadar White House tace ba zata iya tabbatar da sahihancin ikirarin kungiyar ISIS ba cewa ita ta kai harin Garland.

Fadar Shugaban Amurka ta White House ta ce har yanzu lokaci bai yi ba tukun, da za’a yanke hukuncin ko Kungiyar ISIS ce ta kai harin ranar Lahadi a jihar Texas ta kudu maso yammacin Amurka, inda wasu ke zanen barkwancin abin da su ka kira Annabi Muhammad (SAW).

Wannan Kungiya mai tsattsauran ra'ayin, ta yi ikirarin kai harin a gidan rediyonta jiya Talata. Ta ce biyu daga cikin askarawan Daularta ne, su ka kai hari a Garland kusa da Dallas. Ta ce wannan ne harinta na farko a Amurka, kuma wai kadanma aka gani.

Mai magana da yawun Fadar ta White Josh Earnest ya ce Gwamnatin Obama na kaffa-kaffa wajen shelar cewa 'yan ISIS sun shigo Amurka.

"Yace muna shakka saboda haka mu na bukatar karin sani game da gaskiyar lamarin. Akwai masu tsattsauran ra'ayi a fadin duniya, ciki har da masu alaka da ISIS, wadanda ke kokarin amfani da damar da kafafen sada zamunta kan bayar, su yi hulda da mutane a fadin duniya, ciki har da Amurka," a cewarsa.

'Yan sanda sun ce 'yan bindigar su ne Elton Simpson da Nadir Soofi. Mutane biyun sun bude wuta a harabar wurin taron, su ka raunata wani mai gadi kafin 'yan sanda su bindigesu har lahira.

Wasu takardun kotu na nuna cewa an jima ana sa-ido kan take-taken Simpson tun daga shekarar 2006, sannan kuma a shekarar 2010 hukumar bincike ta FBI, ta same shi da laifin shata mata karya, game da niyyarsa ta shiga kungiyar jihadi a Somaliya.

Wata kungiya ce mai suna American Freedom Defence Initiative, ta rajin kare 'yanci a Amurka, ta shirya gasar zanen barkwancin, inda ta yi tayin ladar dala 10,000 ga wanda ya fi kwarewa.

XS
SM
MD
LG