Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka ta ja kunnuwan amurkawa mazauna Afghanistan


John Kerry, sakataren harkokin wajen Amurka
John Kerry, sakataren harkokin wajen Amurka

Biyo bayan yadda kungiyar Taliban suka kara kamari wajen kai hare hare a kasar Afghanistan gwamnatin Amurka ta ja kunnuwan 'ya'yanta dake zaune kasar

Amurka ta ja kunnen Amurkawan dake zaune a kasar Afgahnistan da su kwana cikin shiri saboda mayakan ‘yantawayen kasar na shirin kai hare-haren a kan gidajen baki inda ake sauke mutanen kasashen waje dake birnin Kabul a cikin watan nan.

Sai dai sanarwar tace ba tabbass na ainihin lokaci ko takamammun wuraren da za’a kaiwa farmakin ko ma ainihin fasalin farmakin kansa.

A ‘yan wattanin nan mayakan Taliban sun sha anfani da ‘yan kunar bakin wake wajen kai hare-hare akan mutanen Afghanistan da ‘yan kasashen ketare, ciki harda irin wadanan gidajen na sauke baki.

XS
SM
MD
LG