Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

KALLABI: Menene Dalilin Da Yasa Mata a Arewacin Najeriya Suke Shiga Shan Miyagun Kwayoyi? Yaya Yajin Aikin Yake Shafar Mata a Cikin Gida.


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

A shirin Kallabi na wanan makon zai duba yadda yajin aikin yake shafar Mata a cikin gida a Najeriya. Kungiyoyin kwadago sukan shiga yajin aiki a Najeriya da nufin neman hukumomin su biya musu wadansu bukatu da suka jima suna nema, na baya bayan nan shine yajin aikin da manyan kungiyoyin kwadago a Najeriya suka kira domin neman karin albashi da kuma rage kudin wuta bisa la’akari da tsadar rayuwa da ake fuskanta a kasar. Ta yaya irin wannan matakin yake shafar Mata a cikin Gida?

Sannan shirin zai haska fitila akan yadda Mata a Arewacin Najeriya suke shiga shan miyagun kwayoyi.

Sannan shirin ya tattauna da Helen Bako wadda ta shafe sama da shekaru 23 tana aikin daya jibanci kula da jin dadi da walwalar Al’umma musamman ma tsakanin Iyali a Amurka. Kuma shugabar wata kungiyar wanzar da zaman lafiya ta Mata da ake kira (Nigerian Women against Violence) dake aiki a ciki da wajen Najeriya.

Saurari cikakken shirin da Grace Alheri Abdu ta gabatar:

KALLABI: Menene Dalilin Da Yasa Mata a Arewacin Najeriya Suke Shiga Shan Miyagun Kwayoyi? Yaya Yajin Aikin Yake Shafar Mata a Cikin Gida.
please wait

No media source currently available

0:00 0:23:35 0:00
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG