Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

KALLABI: Ci Gaba Da Tattaunawa Da Masu Kula Da Lamura Akan Tasirin Bikin Ranar Yara Ta Najeriya - Yuni 09, 2024


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Shirin Kallabi na wanan makon zai ci gaba da haska fitila akan Ranar yara a Najeriya, 27 ga watan Mayu na kowacce shekara ranar da kasar ta kebe a matsayin ranar yara da nufin karrama kananan yara daga kasa zuwa matakin sakandare.

Hukumomi a Najeriya sun shafe kusan shekaru sittin suna bikin ranar kananan yara duk shekara, sai dai kamar yadda Malaman da shirin Kallabi ya zanta da su suka bayyana, ranar bata da wani tasiri a rayuwar yaran ko kuma makomarsu a cewar Malama Hauwa Lawal Jibril da Hadiza Tata Gwani, Malaman da suka share sama da shekaru 53 tsakaninsu suna koyarwa, kuma za a iya cewa, sun ga jiya, sun ga yau a fannin ilimi.

Sannan shirin ya tattauna da Zainab Mohammed Bununu wata ‘yar fafatukar kare hakkokin mata matashiya daga jihar Bauchi, inda ta zanta akan koma baya da mata ke samu a fannin siyasa.

Saurari cikakken shirin da Grace Alheri Abdu ta gabatar:

KALLABI: Ci Gaba Da Tattaunawa Da Masu Kula Da Lamura Akan Tasirin Bikin Ranar Yara Ta Najeriya - Yuni 09, 2024
please wait

No media source currently available

0:00 0:22:29 0:00
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG