Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Fashewa A Wani Masallaci A Kano Ta Jikkata Fiye Da Mutane 30, An Kama Wanda Ake Zargi 


Masallacin da wani matashi ya cinna wa wuta a Larabar Abasawa
Masallacin da wani matashi ya cinna wa wuta a Larabar Abasawa

Wata fashewa a wani masallaci dake kauyen gadan, na karamar hukumar gezawa ta jihar kano ya raunata kimanin mutane 35, a yau laraba. Al’amarin ya faru ne da misalin karfe 5 da mintuna 20 na safiya yayin sallar asubahi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, yace sakamakon binciken farko-farko ya nuna cewar man fetur ne ya sabbaba fashewar.

Masallacin da wani matashi ya cinna wa wuta a Larabar Abasawa
Masallacin da wani matashi ya cinna wa wuta a Larabar Abasawa

An kuma kama wanda ake zargi da haddasa fashewar, mai suna Shafi’u Abubakar mai shekaru 38 da haihuwa.

Masallacin da wani matashi ya cinna wa wuta a Larabar Abasawa
Masallacin da wani matashi ya cinna wa wuta a Larabar Abasawa

An ruwaito kiyawa yana cewar, “a bayanin daya baiwa ‘yan sanda, wanda ake zargin ya bayyana wata dadaddiyar takaddamar rabon gado a matsayin dalilnsa na haddasa fashewar. a cewarsa, “ya aikata aika-aikar ne domin nuna adawa da wata dadaddiyar takaddamar danginsa akan rabon gado, kuma yayi haka ne domin a saurare shi.”

Ya cigaba da cewar, “rundunar ‘yan sandan jihar kano na baiwa al’umma tabbacin cewar ana gudanar da cikakken bincike akan lamarin kuma za’a fitar da bayanai anan gaba. a halin yanzu wanda ake zargin na hannun ‘yan sanda, kuma za’a gudanar da cikakken bincike akan lamarin.”

Masallacin da wani matashi ya cinna wa wuta a Larabar Abasawa
Masallacin da wani matashi ya cinna wa wuta a Larabar Abasawa

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG