Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisa Ta Kori  Dan Majalisar New York George Santos


George Santos
George Santos

Majalisar ta kada kuri’a ne a ranar Juma’a don korar dan Majalisar Wakilai daga jam’iyyar Republican George Santos na New York bayan wani rahoto da ya zarge shi da karkata gudummawar yakin neman zabe don amfanin kansa. Shi ne mamba na shida a tarihin Majalisar da abokan aiki suka kore shi.

An dai kada kuri'ar 311-114 ne don tsige shi. Korar ta na bukatar goyon baya daga kashi biyu bisa uku na Majalisar, amma rahoton wani kwamitin Majalisar ya zargi Santos da karya dokar tarayya.

Majalisar Amurka
Majalisar Amurka

Santos ya yi ta kokarin hana korar da aka yi har zuwa lokacin kada kuri'a, inda ya jagoranci kare kansa yayin muhawarar Majalisar, da kuma yayin gudanar da taron manema labarai.

"Ba zan zauna in yi shiru ba," in ji Santos a yayin da 'yan Majalisar suka yi muhawara kan tsige shi da yammacin ranar zaben. “Mutanen gunduma na Uku ta New York ne su ka aiko ni nan. Idan suna son in fice, to lallai ya kamata ku rufe bakinsu sannan ku kada kuri'a."

A cikin korar da aka yi a baya a Majalisar, an kori uku daga ciki ne saboda rashin biyayya ga kungiyar a lokacin yakin basasa. Sauran biyun dai sun faru ne bayan da aka samu ‘yan Majalisar da laifin aikata laifuka a kotun tarayya. Santos ya gabatar da kararsa na ci gaba da zama kan kujerarsa ta hanyar yin kira kai tsaye ga 'yan Majalisar dokokin da suka damu da cewa suna kafa wani sabon salo da zai iya sa korar ta zama ruwan dare.

Santos ya gargadi ‘yan Majalisar cewa, za su yi nadamar tsige wani mamba kafin su iya kare matsayar su.

A farkon watan Maris, kwamitin tsabtace halayya na Majalisar ya ba da sanarwar kaddamar da bincike kan Santos. Sai kuma a watan Mayu, ofishin lauyan Amurka na gundumar Gabashin New York ya tuhumi Santos, yana zarginsa da yaudarar masu ba da agaji, sata daga asusun yakin neman zabensa, da kuma yi wa Majalisa karya. Daga baya masu gabatar da kara za su ƙara ƙarin tuhume-tuhume a cikin sabbin tuhume-tuhume guda 23.

Ana tuhumar sa da laifin satar sunayen masu ba da gudummawar yakin neman zabe sannan kuma ya yi amfani da katin kiredit din su wajen zakulo dubun dubatan daloli da ba a ba shi izinin yi ba. Masu shigar da kara na gwamnatin tarayya sun ce Santos, wanda ya ki amsa laifinsa, ya sanya wasu kudaden a asusun ajiyarsa na banki.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG