‘Yar majalisar dokoki mafi karancin shekaru a Malawi, Fyness Magonjwa, ta shiga gaba wajen yaki da kalubalen da ke hana matasa shiga harkokin siyasa.‘Yar majalisar mai shekara 24 ta ce matasa su na fuskantar manyan kalubale idan suka so tsayawa takara duk da cewa matasa su suka fi yawa a kasar.
Cigaban tattaunawa da Farfesa Ahmed Adamu, masanin tattalin arziki a Najeriya kan yadda za a karfafa shigar matasa harkokin siyasa da shugabanci a Afirka
Natasha Mwansa ‘yar shekara 23 ta samu karbuwa a zukatan ‘yan Zambiya a 2014 lokacin da ta zo ta biyu wani shirin talabijin na kwaikwayon zaben shugaban kasa. Yayin da wasu ke kallon shirin a matsayin nishadi, a wurin Natasha, tamkar tsani ne na kaddamar da facutukarta ta neman shugabanci.
Farfesa Ahmed Adamu, wani masanin tattalin arziki a Najeriya, ya yi bayani kan abubuwan da suke kawowa matasa tarnaki a game da shiga siyasa da shugabanci a Afirka
Amurkawa da dama da za su yi zabe a watan Nuwamba, batutuwan da suka shafi Afirka ba su dame su sosai ba. Sai dai masu sharhi na ganin duk wanda ya yi nasara a zaben, yana da jan aiki na dawowa kimar Amurka a nahiyar ta Afirka.
Har yanzu matsalar cin hanci da rashawa ta na da girma sosai a kasashen nahiyar, ciki har da Ghana. A cewar hukumar kare hakkin dan Adam ta kasar, kashi 20 cikin dari na kasafin kudin kasar ya na silalewa ne saboda matsalar cin hanci da rashawa.
A kowacce shekara, dubban ‘yan Najeriya su na kai rahoton almundahana ga hukumomi. A 2021, kimanin korafe-korafe dubu 140 ne a ka shigar, wanda shi ne lamari mafi yawa a cikin shekaru hudu, a cewar hukumar ta EFCC.
Amurkawa za su yi zabe a watan Nuwamba, batutuwan da suka shafi Afirka ba su dame su sosai ba. Sai dai masu sharhi na ganin duk wanda ya yi nasara a zaben, yana da jan aiki na dawowa kimar Amurka a nahiyar ta Afirka.
Wani matashi a garin Larabar Abasawa dake karamar hukumar Gezawa ya cinnawa wani masallaci wuta yayin da mutane suke sallar asubahi. Rundunar ‘yan sadan jihar ta ce mutumin ya zuba fetur ne, ya banka wuta, sannan ya rufe kofar masallacin. Kimanin mutane 35 ne suka samu raunukan sakamakon al'amarin.
Bayan kawancen soji dake tsakanin kasashen biyu, a yanzu haka kasar ta Rasha ta bullo da wani sabon tsari na koyar da harshen kasarta a makaratun Nijar. Yayin da wasu ‘yan Nijar ke alfahari da shirin, wasu kuwa jan hankalin hukumomin kasar suke yi a game da matsalar da za a iya samu.
Ma’aunin matsalar cin hanci da rashawa a Zambia ya nuna cewa kasar ta samu ci gaba a karon farko cikin shekaru goma, kamar yadda kungiyar Transparency International a kasar ta sanar. Hukumomi a kasar sun ce kwalliya ta fara biyan kudin sabulu a dagewar da suka yi wajen karfafa bin doka da oda.
A lokacin da Martha Ngoye take aiki a matsayin babbar jami’ar al’amuran shari’a a hukumar sufurin jiragen kasa ta Afirka ta Kudu, ta kwarmata badakalar kwangilolin gwamnati na miliyoyin kudi da aka bayar ba bisa ka’ida ba. Sai dai a maimakon a sakanya mata da alheri, sai aka kore ta a wurin aiki.
Domin Kari