Firaiminista Benjamin Netanyahu ya fada ranar Litinin cewa an yi "kuskure mai ban tausayi" a harin da Isra'ila ta kai birnin Rafah da ke kudancin Gaza, wanda ya kona wani sansanin da ke dauke da Falasdinawa da suka rasa matsugunansu, kuma a cewar jami'an yankin, akalla mutum 45 suka rasa rayukansu.