An harbe mutane da dama a Kenya, da ake kyautata zaton wadansu sun rasa rayukansu, yayin da jami'an tsaro suka yi arangama da masu zanga-zanga a fadin kasar domin nuna adawa da tsadar rayuwa da karin haraji, in ji wani jami'in asibiti da kafafen yada labarai na kasar a jiya Laraba.