Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Za A Yi Aiki Da Shari'ar Musulunci Wajen Zana Sabon Tsarin Mulki A Libya


Wazimbabwe wakisubiri kupiga kura ya urais na bunge mjini Harare Julai 31, 2013.
Wazimbabwe wakisubiri kupiga kura ya urais na bunge mjini Harare Julai 31, 2013.

Shugaban wucin gadi yace za a kuma dage dokar da ta kayyade yawan matan da mazajen Libya zasu iya aure

A wurin wani bukin da dubban mutane suka halarta a birnin Benghazi dake gabashin Libya, shugabannin wucin gadi na kasar sun ayyana ‘yanto ta daga mulkin shekaru 42 na marigayi Muammar Gaddafi.

Shugaban Majalisar Mulkin Wucin Gadi, Mustafa Abdel-Jalil ya fadawa gungun mutanen da suka hallara cewa za a yi amfani da tsarin shari’ar Musulunci wajen gina harsashin sabon tsarin mulkin da za a yi amfani da shi a bayan mulkin Gaddafi. Yayi alkawarin cewa za a kakkafa bankunan Islama, sannan kuma za a soke dokar da ta kayyade yawan matan da mazaje a kasar Libya zasu iya aura.

Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-moon, ya bayyana ayyana ‘yantar da Libya a zaman wani lokaci na tarihi bayan mulkin kama-karya na shekara da shekaru. A cikin sanarwar da ya bayar jiya lahadi, Mr. Ban ya sake jaddada goyon bayan Majalisar ga matakan da gwamnatin wucin gadi ta ke dauka na kafa gwamnatin rikon-kwarya tare da gudanar da zabe.

Firayim ministan wucin gadi na Libya mai barin gado, Mahmoud Jibril, yace ana tuntubar sassa da nufin kafa sabuwar gwamnatin rikon-kwarya nan da wata daya, daga nan sai a gudanar da zaben majalisar zana sabon tsarin mulki cikin watanni 8. Za a gudanar da zabubbukan majalisar dokoki da shugaban kasa cikin shekara guda a bayan kafa majalisar zana tsarin mulkin.

Jibril ya bayyana wannan ne a gefen wani taron tattalin arziki da ake yi a kasar Jordan, inda ya bayyana yin murabus dinsa domin bai wa sabbin shugabanni damar jan ragamar kasar Libya zuwa ga tafarkin dimokuradiyya.

XS
SM
MD
LG