Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wata Fashewa Ta Hallaka Mutane 2 A Kasuwar Zamfara


Kano
Kano

Al’amarin daya faru a jiya Talata, ya haddasa tsananin fargaba inda ‘yan kasuwa da masu sayen kaya suka rika gudun neman tsira a kasuwar mai yawan hada-hada.

Fashewar da garin harsashin bindiga ya haddasa a kasuwar Talatar-Mafara dake jihar Zamfara, ta hallaka mutane 2.

Al’amarin daya faru a jiya Talata, ya haddasa tsananin fargaba inda ‘yan kasuwa da masu sayen kaya suka rika gudun neman tsira a kasuwar mai yawan hada-hada.

Wani ganau yace fashewar ta samo asali ne daga wani kanti da ake sayar da bindigogi kirar gida.

Shugaban karamar hukumar Talatar Mafara, Yahaya Yari, ya tabbatar da afkuwar lamarin a yau Laraba.

Ya kuma bayyana cewar an garzaya da mutanen da suka jikkata sakamakon fashewar zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Usman Danfodio dake Sokoto domin samun kulawa.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG