WASHINGTON D.C —
Kamar yadda mujallar Washinton Post ta wallafa, dan takarar shugabancin Amurkar a karkashin jam'iyyar Republican, Donald Trump ya soki Obama ne da Hillary Clinton kan cewa sun ki fitowa fili su bayyanawa mutane cewa hari ne da 'yan ta'addar musulmi suka kai.
Matashin mai shekaru 29 da haihuwa ya kai harinne da babbar bindiga da kuma karama ta hannu a lokacin da ya bude wutar. Wannan dai shi ne harin bindiga mafi muni da aka taba kai wa Amurka a tarihin kasar.