Wasu mutanen da ake kyautata zaton ‘yan kungiyar Boko Haram ne dauke da muggan bindigogi sun kai farmaki talata a kan garin Bama dake arewa maso gabashin Najeriya, suka sako fursunoni sama da 100, da haddasa mutuwar mutane 55, a cewar jami’an Sojan Najeriya. Wadannan hare-haren masu kaifin kishin Islama dauke da muggan makamai, sune na baya-bayan nan a ire-irensu dake kara yin muni tare da barazanar kawar da zaman lafiya a kasar da ta fi kowace kasa yawan jama’a a nahiyar Afrika. An kai hare-haren a wurare da dama a garin Bama dake jihar Bornon Najeriya, wajenda harbe-harbe da fashe-fashen boma-bomai ke cigaba babu kakkautawa tun bayan da kungiyar ta dauki makamai a shekara ta 2010. A daya daga cikin mafiya girma da aka gani a Najeriya, mayakan sun kai wa wani babban kurkukun kasa hari shima, a inda suka sako mutane 105 a cewar jami’an gwamnati.
Sojoji sun ce mutane 55 sun mutu, an sako fursunoni 105, a harin da ‘yan Boko Haram suka kai kan garin Bama

9
A policeman inspects the site to collect evidence in Bama, Maiduguri, Borno State, Nigeria. May 7, 2013.

10
Soldiers enter the gate of Bama Prison, Maiduguri, Borno State, Nigeria May 7, 2013.