Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Salah Da Mane Za Su Sake Karawa, Najeriya Da Ghana Za Su Kece Raini


'Yan wasan Liverpool Sadio Mane, hagu da Mohamed Salah, dama
'Yan wasan Liverpool Sadio Mane, hagu da Mohamed Salah, dama

A watan Fabrairu ‘yan wasan suka hadu a wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar Afrika da Kamaru ta karbi bakunci, inda Senegal ta doke Egypt.

Wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya da za a yi a nahiyar Afirka guda biyar za su tattaro gaggan kasashen nahiyar a ranar Juma’ar nan.

Daya daga cikin wasannin da suka fi jan hankali shi ne sake haduwa da zaratan ‘yan wasan Liverpool Mohamed Salah da Sadio Mane za su sake yi.

Wasan farko za a buga shi ne a binrin Alqahira na kasar Masar.

'Yan wasan Najeriya (Hoto: Twitter Super Eagles)
'Yan wasan Najeriya (Hoto: Twitter Super Eagles)

A watan Fabrairu ‘yan wasan suka hadu a wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar Afrika da Kamaru ta karbi bakunci inda Senegal ta doke Egypt.

Senegal ta lashe kofin bayan doke Egypt da ci 4-2 a bugun fenariti.

Ko da yake, ba wasan na Egypt da Senegal ne kadai zai fi daukan hankali ba, akwai sauran manyan wasannin guda hudu da su ma za a fafata.

'Yan wasan Ghana
'Yan wasan Ghana

Najeriya za ta kara da makwabciyarta Ghana, Kamaru za ta hadu da Algeria.

Kazalika Congo za ta hadu da Morocco, sai kuma Mali ta hadu da Tunisia.

Daga cikin wadannan wasanni, kasashe biyar kadai za su wakilci Afirka a gasar ta cin kofin duniya wacce za a yi a Qatar a wannan shekarar.

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG