Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rikicin Numan: An Tura Masu Bincike Daga Matakin Tarayya


ABUJA: Ministan Tsaron Najeriya Mansur Dan Ali
ABUJA: Ministan Tsaron Najeriya Mansur Dan Ali

Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ce wadanda su ka haddasa rikicin da aka yi kwanan nan a Numan, wanda ya yi sanadin mace-macen mutane da dama, za su dandana kudarsu saboda an kaddamar da binciken zakulo su. Rundunar ta ce muddun aka samu mutun da hannu a wannan rikicin to ko wanene shi zai yaba ma aya zaki.

Hukumar ‘yan sandan Najeriya ta bayyana cewa ta tura masu bincike zuwa Numan don su binciko musabbabin rikicin da aka yi kwanan nan a yankin Numan; su gano wadanda su ka haddasa shi su kuma bayar da shawara kan irin hukuncin da ya dace kansu.

Kakakin Hedikwatar Rundunar ‘Yan sandan Najeriya CSP Jimoh Mooshud ya tabbatar da cewa Sufeto-Janar na ‘yansandan Najeriya ya cika alkawarin da ya yi na tabbatar da cewa an gudanar da bincike a matakin tarayya saboda ya tura masu bincike zuwa inda tashin hankalin ya faru. Hukumar ta ‘yan sanda ta sake yin gargadi ga duk wanda ya sake tayar da zaune tsaye

Wani shugaban Fulani makiyaya a Najeriya, Alhaji Dodo Oroji ya goyi bayan wannan mataki. Y ace muddun ana hukunta masu haddasa fitina to lallai za a takaita tashe-tashen hankula a Najeriya. Shugaban matasan arewacin Najeriya Imrana Wada Nas y ace an sha kafa kwamitin bincike bayan tashin hankali to amma idan aka ga cewa wadanda su ka haddasa shafaffu ne da mai sai a kyale su. Wannan, inji shi, shi ke hana shawo kan fitina a Najeriya.

Ga Hassan Maina Kaina da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:17 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG